in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yan wasan Najeriya zasu ci gaba da samun horon don shiga gasar wasannin Rio Olympics
2016-04-06 16:15:02 cri
Tawagar yan wasan Najeriya 'yan kasa da shekaru 23, ko kuma Dream Team VI, zasu koma ci gaba da samun horo daga ranar Asabar mai zuwa a shirye shiryen shiga gasar wasannin Rio Olympics ta 2016.

Jami'in hukumar kwallon fata na kasar NFF Mohammed Sanusi, ya ce shirye shirye sun yi nisa don kammala shirin bada horon.

Game da shirye wasannin FIFA na mata yan kasa da shekaru 17, wanda za'a gudanar a kasar Jordan a nan gaba cikin wannan shekara, Sanusi ya ce, sun kai babban mataki game da shirye shiryen shiga wasannin.

Yace, zasu samar da kyakkyawan yanayi da kayayyakin da ake buka ga 'yan wasan, sai dai yace sauran shirye shirye ta fuskar tsare tsare yana karkarin ikon kociyan kungiyar wasa na kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China