Shugaban Barcelona Jose Bartomeu, ya fada a ranar Asabar cewa, ba zai yiwu Neymar ya tauna taura biyu a lokaci guda ba.
To sai dai wani jami'in wasanni na ksar Brazil Wagner Ribeiro, ya ce, dan wasan mai shekaru 24 a duniya, bai fidda rai ba wajen gamsar da Barcelona game da kudirinsa na taka leda a wasannin biyu.
Ribeiro, ya ce Neymar yana da burin buga wasannin biyu, kamar yadda aka rawaito shi ya ambata a jaridar Globo newspaper, ya ce sun yi kokarin cimma daidaito da Barcelona, don bashi dama ya zaba cikin wasannin biyu. Amma tuni Neymar, ya yanke kudiri a zuciyar sa na buga wasannin biyu.
Ita dai gasar Copa America za a buga ta a Amurka tsakanin 3 zuwa 26 ga watan Yuni, yayin da a daya bangaren, za'a gudanar da wasannin Olympic a birane 6 na kasar Brazil tsakanin 3 zuwa 20 ga watan Augusta.(Ahmad Fagam)