in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar tattalin arziki da kasuwanci tsakanin Sin da Najeriya a Abuja
2016-03-31 17:59:40 cri


Ranar Laraba 30 ga wata ne, aka yi wani dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar tattalin arziki da kasuwanci tsakanin Sin da Najeriya a birnin Abuja. Wakilinmu Murtala dauke da karin bayani.

Ofishin jakadancin kasar Sin dake Najeriya, gami da ma'aikatar harkokin masana'antu, cinikayya da zuba jari ta tarayyar Najeriya su ne suka shirya wannan dandalin tattaunawa. Manyan jami'an gwamnatocin kasashen biyu, ciki har da jakadan kasar Sin dake Najeriya Mista Gu Xiaojie, da karamar ministar masana'antu, cinikayya da zuba jari ta Najeriya Hajiya A'isha Abubakar.

A yayin tattaunawar, jami'an kasashen Sin da Najeriya, da wasu shugabannin kamfanonin Sin dake Najeriya, da kuma jagororin kungiyoyin 'yan kasuwan Najeriya da dama suka tofa albarkacin bakinsu game da yadda za su yi domin karfafa hadin-gwiwa a fannin kasuwanci da zuba jari.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China