Wata jaridar kasar Brazil ta rawaito babban jami'in tsare-tsaren kungiyar kwallon kafar kasar Gilmar Rinaldi, na cewa duk da kasancewar kungiyar Barcelona ta nuna turjiya game da hakan, yana fatan daga karshe za a cimma matsaya game da baiwa dan wasan damar buga wasa a yayin gasar ta Olympic.
Bisa ka'idojin gasar Olympic dai, ko wace kungiya na da damar sanya 'yan wasa uku da shekarun su suka haura 23 cikin tawagar su, wanda hakan ya baiwa Brazil damar shigar da Neymar mai shekaru 23, da Willian na Chelsea da kuma Miranda dake bugawa Inter Milan wasa cikin tawagar ta.
Za dai a buga gasar wasannin Olympic dake tafe ne tsakanin ranekun 4 zuwa 20 ga watan Agusta mai zuwa, kimanin makwanni 6 bayan kammala Copa America a kasar Amurka. (Saminu Alhassan)