Hukumar kula da wasannin kwallon kafa ta kasar NFF ce ta sanar da nadin, bayan kammala taron kwamitin kwararru na hukumar wasannin a Juma'ar data gabata.
Nadin na Siasia, ya biyo bayan murabus din da tsohon kocin kungiyar wasan kwallon kafar kasar Sunday Oliseh yayi ne daga mukaminsa da safiyar ranar Juma'ar, bisa abinda ya bayyana a matsayin saba yarjejeniya da hukumar kula da wasanninn kwallon kafar kasar tayi.
Hukumar kwallon kafan tace, Siasia zai damu dafawar Salisu Yusuf da kuma Emmanuel Amuneke.(Ahmad Fagam)