in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta bude sansanin horas da 'yan wasa mata a gabannin wasan share fagen cin kofin kasashen Afrika
2016-03-01 14:50:37 cri
A ranar Talatar nan za'a bude sansanin horas da 'yan wasa mata na Najeriya, domin shiga zagaye na biyu na gasar share fagen cin kofin wasannin mata na Afrika da aka shirya gudanarwa cikin wannan shekara.

Hukumar kula da wasan kwallon kafan kasar NFF ce ta sanar da hakan a ranar Litinin din data gabata, tace kimanin 'yan wasan 40 ne kocin horas da 'yan wasan Florence Omagbemi ya gayyata domin shiga shirin bada horon wanda za'a gudanar a Abuja.

Najeriya, wacce ta samu nasarar zama zakara har sau 7 a wasnnin mata a nahiyar, zata kara ne da takwarorinta na kasashen Senegal da Guinea a watan Maris, da kuma ranakun 4 da 12 na watan Aprilu.

Za'a gudanar da wasannin cin kofin Afrika na mata ne na shekarar 2016 a Jamhuriya Cameroon a watan Nuwamba.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China