in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci a gudanar da zabe cikin lumana a DRC
2016-02-17 11:15:38 cri
MDD da kungiyoyin shiyyoyi 3 sun bukaci jam'iyyun siyasar jamhuriyar demokuradiyyar Congo DRC da su tabbatar da cewar, an gudanar da zabukan kasar cikin kwanciyar hankali.

Wannan kiran na hadin gwiwa ne tsakanin kungiyar hada kan kasashen Afrika AU, da MDD, da kungiyar tarayyar turai EU, da kuma kungiyar kasashe masu magana da Faransanci IOF.

Sanarwar ta bayyana cewar, kungiyoyin suna ci gaba da bibiyar al'amurran dake wakana a kasar mai fama da rikici, musamman game da zaben kasar dake tafe.

Kungiyoyin hudu sun dauki batun zaben kasar da muhimmanci, domin ganin an gudanar da shi cikin kwanciyar hankali, wanda ake sa ran zai kasance zakaran gwajin dafi wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaban kasar.

Sanarwar ta ce kungiyoyin sun bukaci masu ruwa da tsaki a harkokin siyasar congo da su yi biyayya ga kundin tsarin mulkin kasar, don tabbatar da yin zaben cikin nasara, da samun dauwamamman zaman lafiya da kuma kafuwar tsarin demokuradiyya a kasar.

Kaza lika, kungiyoyin hudu sun bukaci bangarorin dake hamayya da juna a DRC, da su warware duk wata takaddama ta hanyar bin ka'idojin shari'a.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China