160121-Zambia-ta-doke-Zimbabwe-yayin-da-Uganda-ta-buga-kunnen-doki-da-Mali-a-gasar-CHAN-zainab.m4a
|
Dan wasan Zambia Isaac Chansa ne ya jefa kwallo daya tilo da aka ci a wasan a ragar Zimbabwe cikin minti na 58, haka kuma aka tashi, duk da irin yunkurin da 'yan wasan Zimbabwe suka yi na farke kwallon.
A dai rukunin na D, Uganda ta buga kunnen doki biyu da biyu da kasar Mali.
A kuma ranar Juma'a Uganda za ta buga wasa na gaba da Zimbabwe, yayin da ita kuma Zambia za ta kara da kasar Mali.(Saminu Alhassan)