in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hira da Dr. Sheriff Ghali Ibrahim, malami ne dake koyarwa a fannin kimiyyar siyasa da alaka ta kasa da kasa a jami'ar Abuja
2015-11-30 14:48:29 cri


Shekarar da muke ciki shekara ce ta cika shekaru 15 da aka kafa dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka wato FOCAC, kuma daga ranar 2 zuwa 5 ga wata mai zuwa wato Disamba, za a kira taron koli na dandalin a kasar Afirka ta kudu, wannan ne karo na farko da aka shirya taron koli a babbar nahiyar Afirka, shugaban kasar Sin Xi Jinping, shugaban kasar Afirka ta kudu Jacob Zuma, da babban sakataren MDD Ban Ki-Moon da kuma shugabanni na wasu kasashen Afirka, da jami'an wasu kungiyoyin kasa da kasa za su halarci taron.

Tun daga shekarar da ta wuce dai, sau da yawa kasashen Afirka suka bayyana fatansu na kara matsayin wannan taro daga taron ministoci zuwa na koli. Saboda haka, an biyan bukatun bangaren Afirka, taron din na karfafa hadin kai irin na samun moriyar juna da nasara tare a tsakanin Sin da kasashen Afirka, da kara imanin kasashen Afirka da kasa da kasa kan bunkasuwar nahiyar Afirka, kana zai sanya kasashen duniya su kara mayar da hankali da zuba jari kan Afirka.

Game da wannan babban taron dai sashenmu na Hausa na CRI mun shirya jerin shirye-shirye, inda muka zanta da wasu jami'ai, masana na Sin da Afirka. A yau ne za mu kawo muku na farko daga cikinsu, inda wakilinmu dake birnin Abuja na kasar Najeriya Murtala ya zanta da Dr. Sheriff Ghali Ibrahim, malami ne dake koyarwa a fannin kimiyyar siyasa da alaka ta kasa da kasa a jami'ar Abuja. To, yanzu sai ku biyo mu cikin zantawar tasu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China