Taron kungiyar kasashe masu amfani da harshen Faransanci karo na 16 zai gudana a kasar Madagascar daga ranar 15 zuwa 20 ga watan Nuwamban shekarar 2016, in ji kwamitin shirye shirye na kungiyar a ranar Litinin. Bisa taken "Bunkasa musanya da ci gaba mai dorewa", dandalin zai tattara shugabannin kasashe da gwamnatoci da suka fito daga kasashe mambobi guda 80 na kungiyar. Kuma a karon farko ne tsibirin na Madagascar zai karbi bakuncin wannan taro na kungiyar. (Maman Ada)