in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya yi kira da a dauki matakin da za'a sha kan matsalar bakin haure
2015-10-10 18:16:27 cri
Wakilin kasar Sin a MDD Liu Jieyi a jumma'an nan yayi kira ga kasashen duniya da su dauki matakin da za'a iya shawo kan matsalar bakin haure da ke bi ta bahar Rum, ta hanyar mai da hankali akan talauci, rashin kwanciyar hankali a cikin al'umma da kuma fadace fadce da ake fuskanta.

Liu Jeiyi wanda shi ne wakilin din din din a MDD mai wakilai 15 yayi wannan kiran ne a taron kwamitin tsaro bayan da aka amince da shawarar daukan matakai na hana safaran mutane da jigilar bakin haure ta kan bahar Rum da ya ratsa ta Libya.

A cewar wani rahoton da ofishin kula da 'yan gudun hijira na MDD ya zuwa watan Agustan wannan shekarar kawai yan gudun hijira da bakin haure da suka tsallake bahar Rum sun wuce 300,000. Wadansu 2,500 kuma a cewar rahoton da suka hada da bakin hauren da 'yan gudun hijira da ma 'wassu daga kasar ta Libya sun mutu ko sun bace a kokarin da suke yi na tsallakawa zuwa yankin Turai.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China