in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya ce ba za a rage darajar Yuan domin bunkasa fitar da kayayyaki ba
2015-09-09 18:50:21 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya ce ba za a aiwatar da manufar rage darajar kudin kasar Sin na Yuan domin bunkasa hada-hadar fitar da kayayyaki ba. Hasali ma a cewar sa Sin ba ta da niyar bude kofar takarar kudade tsakanin ta da sauran kasashen duniya.

Mr. Li wanda ya bayyana hakan yayin taron 'yan kasuwa na Davos wanda ya gudana a Arewa maso Gabashin kasar Sin, ya bayyanawa mahalarta taron cewa rage darajar kudin Yuan domin bunkasa fidda kayayyaki, ba manufa ba ce da ta dace da tsarin gyaran fuskar tattalin arziki da Sin ke aiwatarwa.

Daga nan sai ya jaddada cewa kasar Sin ba ta fatan ci gaba da rage darajar kudin na Yuan. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China