in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A karon farko Sin ta kasance kasa ta farko da ke jawo jarin waje a bara
2015-09-09 09:40:57 cri
Jiya ne a birnin Xiamen da ke nan kasar Sin hukumar kula da harkokin cinikayya da bunkasuwa ta MDD ta fitar da wani rahoto game da harkokin zuba jari a duniya a shekarar 2015, inda ta bayyana cewa, yawan jarin da kasashen waje suka zuba ga kasar Sin kai tsaye a shekarar 2014 ya kai dala biliyan 129, wanda ya karu da kashi 4 cikin dari bisa na makamancin lokacin shekarar 2013, lamarin da ya baiwa kasar Sin damar zarce kasar Amurka wajen jawo jarin kasashen waje a duniya a karon farko.

A cewar rahoton, kasashe ko yankuna 10 da suka fi jawo jarin kasashen waje a duniya a shekarar 2014 sun hada da Sin, yankin Hongkong, Amurka, Britaniya, Singapore, Brazil, Canada, Australia, Indiya da kuma Netherlands.

Shugaban sashen kula da harkokin zuba jari da kamfanoni na hukumar Zhan Xiaoning ya bayyana cewa, wannan rahoto ya shaida cewa, Sin tana daya daga cikin manyan kasashe ko yankunan da suka fi jawo hankulan masu sha'awar zuba jari a duniya, kana Sin ta kara taka muhimmiyar rawa wajen inganta harkokin zuba jari a duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China