in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin da kasashen Afrika za su yi taro a Afrika ta kudu a watan Disamba
2015-09-04 13:17:27 cri
Babban taro na shugabannin kasashen Afrika da kasar Sin zai gudana ne a kasar Afrika ta kudu a farkon watan Disamba kamar yadda ministocin harkokin wajen kasashen biyu duka suka tabbatar a ranan Jumma'an nan a nan birnin Beijing.

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwaransa na Afrika ta kudu Maite Nkoana-Mashabane da suka sanar da hakan tare, sun ce shugabannin kasashen biyu duk sun amince a daga matsayin taron ministocin na hadin gwiwwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika karo na 6 zuwa babban taron.

Shugabannin kasashen guda biyu har ila yau za su gayyaci sauran shugabannin kasashen Afrika da su halarci taron wanda zai gudana a ranakun 4-5 na watan Disamban bana. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China