A labarin da gwamnati ta bayar, an ce, jirgin na dauke da mutane 456, kuma kawo yanzu, 14 daga cikinsu ne kawai suka tsira da rayukansu, a yayin da ake cikin neman sauran mutane 46.
Har wa yau, wani jami'in soja ya bayyana cewa, tun bayan da aka fara gudanar da bincike cikin jirgin a Jumma'ar nan da ta wuce, an gano gawawwaki da dama. Domin kiyaye mutumcin matattu, an yi hankali sosai wajen kaurar da gawawwaki, domin kaucewar lalacewarsu. (Lubabatu)