in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya bukaci a kara zuba jari a fannin rigakafin cutar ciwon zazzabin cizon sauro
2015-04-26 16:52:43 cri
Babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa, da su kara zuba jari a aikin gano dabarun rigakafi, da jinyar cutar zazzabin cizon sauro ko Maleriya, yana mai cewa ya kamata a gaggauta gano sabbin hanyoyi, da magungunan rigakafi, da na maganin cutar ta zazzabin cizon sauro.

Bugu da kari, Ban Ki-moon ya ce ya kamata a samarwa wadanda suke da bukatu karin kayayyakin kariya daga cutar ta Maleriya, da kuma koyar da jama'a karin fasahohin magance yaduwar sauro. A cewar sa wadannan ayyuka na bukatar karin kudade daga gamayyar kasa da kasa, ta yadda za a iya taimakawa kasashe mafiya fama da talauci kyautata tsarin kiwon lafiyar su yadda ya kamata.

Jiya Asabar ne dai ranar cutar Maleriya ta duniya, a kuma wannan rana ne Mr. Ban ya bayyana irin ci gaban da aka samu a aikin rigakafi, da na hana yaduwar ciwon na Maleriya tsakanin kasashen duniya.

Wani rahoton hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO ya nuna cewa, tun daga shekarar 2000 ya zuwa yanzu, adadin wadanda suka rasa rayukansu sakamakon kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro ya ragu da kimanin kaso 50 bisa dari.

Rahoton ya kara da cewa an samu wannan nasara ne sakamakon kwarewa da aka nuna a bincike game da cutar zazzabin cizon sauro, da kuma amfani da fasahohin jinya masu nagarta, haka kuma a yanzu haka an kara samar da kayayyakin kandagarki masu amfani kwarai da gaske. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China