in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: An gudanar da karashen zaben gwamnonin cikin tsauraran matakan tsaro
2015-04-26 16:07:30 cri
Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya INEC, ta gudanar da ragowar zaben gwamnoni a wasu mazabun kasar da ba a kai ga kammalawa ba, yayin zaben ranar 11 ga watan nan.

Rahotanni sun bayyana cewa an gudanar da ragowar zabukan ne a jihohin Abia, Imo, Taraba, da Delta da kuma jihar Kogi.

An ce cincirindon jama'a sun cika rumfunan zaben na jiya Asabar a jihar Taraba, wadda ke Arewa maso Gabashin kasar. Inda aka kada kuri'u a rumfuna 218 dake kananan hukumomin jihar 10. Yayin da kuma jami'an tsaro ke sanya ido a dukkanin wuraren da zaben ya gudana, domin kaucewa aukuwar tashin hankali.

A dai jihar ta Taraba, rundunar 'yan sanda ta kafa dokar hana zirga-zirga tun daga karfe 8 na safe zuwa karfe 5 na yammacin ranar ta Asabar, a wani mataki na tabbatar da tsaro a ranar zaben.

A daya hannun kuma INEC ta bukaci 'yan sanda da su dakatar da zirga-zirgar 'yan siyasa, da jami'an gwamnati, duka dai da nufin kammala zaben cikin kyakyawan yanayi. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China