in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin mata sun yi kira da a kara samar da daidaici tsakanin jinsuna
2015-03-01 16:23:42 cri
Shugabannin matan duniya fiye da 60 sun yi kira a ranar Asabar, a yayin wani zaman taron mata da MDD ta shirya a birnin Santiago, hedkwatar kasar Chili, da a kara daukar nargartattun matakai domin cimma burin samun daidaici tsakanin mabanbantan jinsuna nan zuwa shekarar 2030.

Shugabar kasar Chili, Michelle Bachelet da sakatare janar na MDD Ban Ki-moon sun cimma rattaba hannu bayan kammala taron na kwanaki biyu kan wani kundi mai taken "Yin kira ga aiwatarwa"

Ana kira ga maza da mata da su gaggauta kawo sauye sauye domin kai ga cimma wannan buri na daidaici, ba wai cikin shekaru da dama masu zuwa ba amma cikin dan kankanin lokaci, in ji madam Michelle Bachelet a cikin wani jawabinta na rufe taron na manyan jami'ai kan "matan dake shugabanci da daukar matakai"

Zaman taron na da manufar bullo da hanyoyin gaggauta ci gaba kan maradun da aka tsai da a yayin babban taron duniya na mata karo na hudu, da aka shirya a shekarar 1995 a birnin Beijing na kasar Sin.

Mista Ban Ki-moon ya bayyana cewa duniya ba za ta cimma burinta ba dari bisa dari idan aka nuna wariya ga kashi 50 cikin 100 na al'ummarta, tare da kara bayyana cewa yanzu lokaci ya yi na daukar mataki domin cike wannan gibi, da fuskantar kalubale da kuma zuba jari ga mata da 'yan mata. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China