in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD:shekaru 70 da ceto Yahudawa daga Auschwitz Birkenau
2015-01-29 14:52:33 cri

MDD ta gudanar da wani biki a cibiyarta dake birnin New York a jiya Laraba, don tunawa da mutanen da suka rasa rayukan su sakamakon kisan kiyashi, da kuma cika shekaru 70 da ceto Yahudawa daga Auschwitz Birkenau.

An dai kebe ranar 27 ga watan Janairun kowace shekara, a matsayin ranar tunawa da mutane da suka mutu, a sakamakon kisan kiyashin da sojojin Nazi suka aiwatar. A makamanciyar wannan rana a shekarar 1945 ne dai sojojin kawancen kasa da kasa, suka ceto Yahudawan da aka yi garkuwa da su a gidan tsare mutane na Auschwitz Birkenau. A kuma bana MDD ta jinkirta bikin zuwa 28 ga wannan wata, sakamakon hadarin kwararar dusar kankara da aka samu a arewa maso gabashin kasar Amurka cikin wannan mako.

Da yake jawabi don gane da bikin, babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya ce ra'ayin nuna kyama da nuna kiyayya ga Yahudawa ba abu ne da za a amince da shi ba a dukkanin fadin duniya. Kana ya yi kira ga kasashen duniya da su kawar da rashin jituwa daga tushe.

A nasa jawabi shugaban kasar Isra'ila Reuven Rivlin, ya ce cikin manyan dalilin kafa MDD har da daukar matakan tabbatar da magance aukuwar irin wancan kisan kiyashi a nan gaba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China