in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yang ya gana da shugabannin kasashe da ke halartar bikin baje kolin kasar Sin da kasashen Asiya da Turai
2014-09-01 16:01:43 cri
Mataimakin firaministan kasar Sin Wang Yang ya gana da firaministan kasar Kazakhstan Karim Kajimqanüly Masimov, firaministan kasar Kyrgyzstan Dzhoomart Otorbaev da kuma mataimakin shugaban majalisar dokokin kasar Georgia Zviad Dzidziguri da suke halartar bikin baje koli na kasar Sin da kasashen Asiya da Turai.

Yayin da yake ganawa da Masimov, Wang Yang ya bayyana cewa, an samu babban ci gaba ta fuskar fahimtar juna da hadin gwiwa a tsakanin Sin da Kazakhstan, wadanda suka kawo moriya ga jama'ar kasashen biyu, tare da bada gudummawa wajen samun zaman lafiya da bunkasuwa a yankunansu.

Yayin da yake ganawa da Otorbaev kuwa, Wang Yang ya ce, kamata ya yi kasashen Sin da Kyrgyzstan su kara yin hadin gwiwa don bullo da sabbin fannonin samun bunkasuwar cinikayya a tsakaninsu.

Kana a ganawar da Wang Yang ya yi da Dzidziguri, ya ce, kasar Sin ta zama kasa ta biyar wajen yin ciniki da kasar Georgia, kana kasa ta uku wajen zuba jari ga kasar. Kuma kasar Sin za ta sa kaimi ga kamfanonin kasar da su zuba jari da yin ciniki a kasar Georgia. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China