Kafin wannan, Masar ta tattauna game daba da shawarar kara wa'adin tsagaita bude wuta zuwa awoyi 120. Game da wannan batu, Isra'ila ta nuna amincewa, yayin da kungiyar Hamas ta bayyana cewa, za ta ci gaba da kai hari idan Isra'ila ba za ta kawar da shinge da ta dasa ajanye sojojinta wadanda ke yi ma yankin Gaza kawanya ba. Bayan kawo karshen wa'adin tsagaita bude wuta a yau kuma, ya zuwa karfe 10 da minti 30 na safiyar yau, an harba roka kimanin 20 daga yankin Gaza zuwa Isra'ila. Daga bisani, kungiyar PIJ ta sanar da daukar alhakin lamarin. Abin da ya sanya Isra'ila ta yi ramuwar gayya da hare-haren jiragen saman yaki daga bisani.(Fatima)