An ce tun da fari kwamitin tsaron kasar Netherlands ya mika akwatunan nadar bayanan guda biyu, ga cibiyar binciken hadarin jiragen sama ta kasar Ingila ne, da fatan masana a fannin hadarin jiragen sama na cibiyar za su gudanar da bincike, da nazarin da ya dace.
Ban da wannan, kakakin fadar firaministan kasar Ingila ya bayyana cewa, kasarsa ta ja hankalin dakarun sa kai dake gabashin Ukraine, da su datakar da tada zaune tsaye, tare kuma da fatan gwamnatin kasar Ukraine, za ta kokarta wajen samar da tsaro ga tawagar masu bincike ta Netherlands da Australia. (Zainab)