131108-ziyara-a-masallacin-Doudian-Lubabatu.m4a
|
Kasar Sin kasa ce da ke da dimbin musulmi da yawansu ya kai sama da miliyan 20. A birnin Beijing, babban birnin kasar Sin ma, ba a rasa musulmi ba, inda a sabili da haka ake samun masallatai da dama da yawansu ya kai sama da 70.
Daga cikin masallatai na birnin Beijing, masallacin da ke yankin Doudian a yanzu haka ya kasance mafi girma, wanda Fadinsa ya kai muraba'in mita 12142, kuma yana iyar karbar musulmi 1500 a lokacin yin sallah.
To, sai a biyo mu zuwa masallacin na Doudian.