in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Maroco ta dauki niyyar kare kayayyakin tarihin Afrika
2013-03-08 15:35:06 cri
Ofishin ministan al'adun kasar Maroco da asusun cigaban kayayyakin tarihin kasa da kasa na Afrika sun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar hadin gwiwa a fannonin kare kayayyakin tarihi da harkar bunkasa al'adu, a wani labari da kamfanin dillancin labarai na MAP ya ruwaito jiya.

Sanya hannu kan wannan yarjejeniya ya biyo bayan wani taron da ya gudana kwanan nan a birnin Rabat, wanda ya samu halartar manyan ofishin ministan tare da tawagar dake kunshe da darektan asusun kayayyakin tarihin kasa da kasa na Afrika, mista Webber Ndoro, darektan kayayyakin tarihi a ofishin ministan al'adun kasar Afrika ta Kudu, Irwin Langeveld da kuma jami'in dake kula da dangantakar kasa da kasa a asusun Afrika, mista Inge Herbert, a cewa wannan sanarwa ta ofishin ministan al'adun kasar Maroco.

A cewar darektan kayayyakin tarihi a ofishin ministan al'adu, Abdellah Alaoui, wannan yarjejeniya tana bude babbar kofa wajen yin musanyar kwarewar Maroco tare da sauran kasashen Afrika, musammun wadanda dake kudu da hamadar Sahara a fannonin karewa da kuma shigar da muhimmancin kayayyakin tarihi da ba da kulawa ga wuraren tarihi na duniya na kungiyar UNESCO. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China