• Han Qide ya je ofishin jakadan kasar Nijeriya dake kasar Sin don nuna jejeto ga rasuwar tsohon shugaban kasar Nijeriya Yar'Adua
More>>
Sharhi
• Allah ya yi ma shugaban Najeriya Alhaji Umaru Musa Yar'Adua rasuwa
Ran 5 ga wata da dare, kakakin shugaban kasar Najeriya ya sanar wa kafofin watsa labaru cewa, shugaban Najeriya Alhaji Umaru Musa Yar'Adua da ya shafe tsawon lokaci yana fama da rashin lafiya ya rasu a daren wannan rana da karfe 9 da rabi a fadar shugaban kasar da ke birnin Abuja, hedkwatar kasar. Shekarunsa 58 ne kawai a duniya.
More>>
Labarai
• Ban Ki-Moon ya nuna juyayi game da rasuwar tsohon shugaban kasar Nijeriya Umaru Yar'Adua
• Shugaban kasar Sin ya nuna alhini ga rasuwar marigayi shugaba Umaru Yar'Adua na Nijeriya
• (Sabunta)Goodluck Jonathan ya yi rantsuwar kama mukamin shugabancin kasar Nijeriya
• Goodluck Jonathan ya yi rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasar Nijeriya a ran 6 ga wata
• Kasar Sin ta nuna alhini a game da rasuwar shugaban kasar Nijeriya
More>>
Takaitaccen tarihin marigayi Yar'adua
Allah ya yi wa shugaban kasar Najeriya Alhaji Umaru Yar'Adua rasuwa a jiya Laraba a birnin Abuja bayan ya yi fama da doguwar rashin lafiya.

Marigayi Yar'Adua ya fito ne daga jam'iyyar PDP inda a karkashin jam'iyyar ce ya samu nasarar zama shugaban kasar Najeriya a shekara ta 2007 kuma ya kasance shugaba na farko dake da ilimin digiri a kasar.

An haifi marigayin ne a cikin zuriyar dake da asali ta fuskar siyasa a Arewacin jihar Katsina a shekara ta 1951.

Haka zalika mahaifin marigayin ya taba zama minista a lokacin gwamnatin farko bayan samun yancin kan Najeriya daga turawan mulkin mallaka a shekara ta 1960 kuma a wanccen lokaci dan'uwansa ya kasasnce shi ne na biyu a kasar a lokacin da Olusegun Obasanjo ya ke rike da mukamin shugaban mulkin soji a kasar a shekara ta 1970.

Marigayi Yar'Adua ya taba zama malamin chemistry wato sanin halittu da dabarun hada magunguna kuma ya taka rawa sosai a bangaren kasuwanci daga bisani sai shiga harkokin siyasa dumu dumu a cikin shekara ta 1980.

Haka kuma ya dan yi fice a cikin kasar kafin tsohon shugaban kasar Obasanjo ya tsaida shi a matsayin dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar jam'iyyar PD.P. a karshen shekara ta 2006, ....

© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China