Wei Jianguo ya ce, bayan da aka yi taron koli kan sha'anin hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika, matsakaicin yawan cinikin bangarorin biyu tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika ya kan karu da sama da kashi 40 cikin 100 a ko wace shekara. Mr. Wei ya yi nuni da cewa, yanzu, ana samun bunkasuwar cinikin bangarorin biyu cikin daidaito, kuma kayayyakin da Sin ta kan shigar da su daga kasashen Afrika sun dace da samun bunkasuwar kasar Sin, kana kasar Sin ita ma ta kan fitar da kyawawan kayayyaki masu araha da ke samun karbuwa ga jama'ar Afrika zuwa kasashen Afrika, an ce, hadin gwiwa kan harkokin cinikayya tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika zai kawo sakamako na hadin gwiwa da samun moriyar juna. (Bako)

