Ayyukan soja da za a gudanar a kudancin kasar Afghanistan za su kyautata halin tsaro na kasar

A ran 7 ga wata, babban kwamandan sojojin Amurka dake a kasar Afghanistan Stanley McChrystal ya bayyana cewa, ayyukan soja da za a gudanar a jihar Helmand dake kudancin kasar Afghanistan za su bayyana wa jama'ar kasar Afghanistan cewa, gwamnatin kasar Afghanistan tana fadada wuraren da take iya kiyaye zaman lafiya.
A wannan rana a birnin Kabul, Mr McChrystal ya gudanar da wani taron manema labaru, inda ya ce, ayyukan soja da za a gudanar za su mai da hankali kan hadin gwiwar dake tsakanin sojoji da jama'a, ba ma kawai za a kyautata halin tsaro a wannan yanki a nan gaba ba, hatta ma za a inganta karfin gwamnatin kasar Afghanistan a fannin aiwatar da ayyukanta.(Zainab)