Liu Guijin ya jaddada cewa, Sin ta sa lura kan batun Darfur sosai, kana ta taka muhimmiyar rawa wajen warware batun. Sin ta nuna goyon baya da shiga ayyukan kiyaye zaman lafiya a yankin Darfur, wadda ta kasance kasa ta farko a waje da nahiyar Afirka da ta tura sojojin kiyaye zaman lafiya zuwa yankin Darfur don gudanar da aiki. Ya nuna cewa, Sin ta dora muhimmanci kan ba da taimako ga yankin Darfur wajen bunkasa tattalin arziki da kuma kyautata halin jin kai, ya zuwa yanzu, ta riga ta samar da kayayyakin gudummawa da darajarsu ta kai kudin Sin Yuan miliyan 160 ga wannan yanki. Liu Guijin ya bayyana cewa, Sin tana son ci gaba da yin kokari tare da bangarori daban daban da abin ya shafa don warware batun Darfur tun da wuri.
Ban da wannan, shugaban kwamitin kungiyar AU Jean Ping ya bayyana cewa a wajen taron shawarwari tsakanin kungiyoyin fararen hula na yankin Darfur, shigar kungiyoyin za ta yi babban tasiri ga bangarorin daban daban da suke yaki da juna a yankin wajen samun sulhuntawa.(Zainab)

