Tambayar da za mu amsa a wannan mako ta fito ne daga hannun Iliya Abbas, daga Maiduguri, jihar Borno, tarayyar Nijeriya. A cikin wasikar da malamin ya aiko mana, ya ce, mun san dai yanzu ana wasannin Olympic tsakanin nakasassu a birnin Beijing, babban birnin kasar Sin, wannan abu mai kyau sosai ga nakasassu na kasa da kasa, to, tambayata ita ce, shin yaya gwamnatin kasar Sin ke kula da nakasassun kasar?
To, malam Iliya Abbas da dai sauran masu sauraronmu, yanzu a gyara zama a sha bayani dangane da halin da nakasassu ke ciki a kasar Sin. Yanzu akwai nakasassun da yawansu ya kai sama da miliyan 80 a nan kasar Sin, wadanda suka dau kashi 6% na yawan al'ummar kasar Sin baki daya.
1 2 3
|