Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-16 10:54:19    
Kasar Sin ta yi kira ga kasar Iran da ta amsa shirye-shiryen da aka tsara ta cikakkun hanyoyi kan batun nukiliya na kasar Iran

cri
Ran 15 ga wata, mataimakawa na ministan harkokin waje na kasar Sin Mr. Cui Tiankai da ke ziyarar aiki a kasar Iran ya yi wa kafofin yada labaru bayanin cewa, kasar Sin tana fatan kasar Iran za ta yi amfani da zarafi za ta amsa shirye-shiryen da kasashe 6 suka bayar kan batun nukiliya na kasar Iran.

Mr. Cui ya kara da cewa, har kullun bangaren kasar Sin yana tsayawa tsayin daka kan warware batun nukiliya na kasar Iran cikin lumana ta hanyar yin shawarwarin diplomasiyya. Saboda haka, bangaren kasar Sin yana fatan bangaren kasar Iran zai amsa shirye-shiryen da kasashen 6 suka bayar ta cikakkun hanyoyi, a sa'i daya kuma, yana fatan sauran bangarorin da abin ya shafa za su dauki matakan da suka wajaba wajen samar da sharadi ga mayar da shawarwari.(Tasallah)