Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-09-21 10:17:43    
WFP ta yi kira ga kasashen duniya da su samar wa yaran Angola taimako

cri
A ran 20 ga wata hukumar tsara shirin samar da abinci ta kasa da kasa ta yi kira ga kasashen duniya da su samar wa kasar Angola taimakon kudin dolar Amurka kimanin miliyan 30 domin ba da taimako ga yaran kasar da ke fuskantar yunwa da ciwace-ciwace iri iri.

A wannan rana, hukumar tsara shirin samar da abinci ta kasa da kasa ta bayyana cewa, domin hukumar ba ta da isashen kudi, kuma babu sauran hanyar da za ta iya zaba, sai ta rage yawan kudaden da take samar wa kasar Angola.

Yanzu, hukumar tana aiwatar da shirin samar da abinci ga yara dubu dari 4 wadanda suke zaune a kudu maso yammancin kasar Angola. Amma yanzu hukumar tana bukatar dalar Amurka kimanin miliyan 30 cikin gaggawa ta yadda za ta iya ci gaba da aiwatar da shirin nan har karshen shekara mai zuwa. (Sanusi Chen)