Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-22 17:06:17    
Najeriya za ta mika wa zababbiyar gwamnatin Liberia Charles Taylor

cri
A ran 21 ga wata, kamfanin dillancin labaru na Najeriya, wato NAN ya bayar da labari cewa, gwamnatin kasar Najeriya za ta mika wa zababbiyar gwamnatin kasar Liberia tsohon shugaba Charles Taylor na kasar Liberia wanda ke neman mafakar siyasa a kasar Najeriya.

Wannan labari ya tsamo maganar da ministan harkokin waje na kasar Najeriya Mr. Oluyemi Adeniji ya yi, cewar idan zababbiyar gwamnatin kasar Liberia da za ta ci zaben da za a yi a watan Oktoba na shekarar nan ta kai Charles Taylor kara, kuma ta nemi kasar Najeriya da ta komar da Charles Taylor. Kasar Najeriya za ta komar da Charles Taylor ga gwamnatin kasar Liberia, kuma a sa'i daya, za ta sanar wa kungiyar hada kan tattalin arzikin yammacin kasashen Afirka, wato ECOWAS da Tarayyar Afirka, wato AU da wannan labari. (Sanusi Chen)