Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-19 09:53:57    
An yi muhawara a kan shirin kudurin habaka kwamitin sulhu da gamayyar Afirka ta gabatar

cri

A ran 18 ga wata, an yi babban taron MDD, inda aka yi muhawara a kan shirin kudurin habaka kwamitin sulhu da gamayyar kasashen Afirka ta gabatar a makon jiya.

A gun muhawarar, wakilan kasashen Nijeriya da Masar da Aljeriya da Burkina faso sun yi jawabi, inda suka nemi a kawo karshen rashin kasancewar zaunannun kujerun kasashen Afirka a kwamitin sulhu, kuma suka yi kira ga kasashe daban daban da su goyi bayan shirin kudurin da gamayyar Afirka ta gabatar.

A cikin shirin kudurin da gamayyar Afirka ta gabatar, ana neman kara zaunannun kasashe 6 wadanda ke da ikon nuna rashin amincewa da kuma kasashe 5 da ba na dindindin ba a kwamitin sulhu.

A halin yanzu, gamayyar Afirka ba ta fitar da kasashen da za su nemi kujerar dindindin a kwamitin sulhu a madadin kasashen Afirka ba. Amma kasashen Masar da Afirka ta kudu da Nijeriya da kuma Kenya sun riga sun nuna sha'awarsu game da aikin nan.(Lubabatu Lei)