Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-14 20:19:47    
Kasashen Afirka za su gina wata babbar koriyar katanga a yankin Sahara

cri

A ran 13 ga wata a birnin Dakar, babban birnin kasar Senegal, shugaban kasar Abdoulaye Wade ya bayyana cewa, shugabannin kasashen Afirka sun yarda da shawarar da shugaban zartaswa na kawancen kasashen Afirka kuma shugaban kasar Nijeriya Obasanjo ya gabatar, sun yanke shawarar gina wata babbar koriyar katanga a yankin Sahara.

Mr Wade ya ce, za a gina koriyar katanga mai fadin kilomita 5 daga birnin Dakar na kasar Senegal zuwa kasar Djibouti wadda ta ratsa kasashen Senegal da Mali da Niger da Chadi da Sudan da Habasha da kuma Djibouti. Sabo da haka ne, kasashen da abin ya shafa za su bayar da kayayyaki da kudi da kuma mutane domin dasa itace, ta yadda za a hana yaduwar hamadar Sahara da moriyar 'ya 'yansu.(Danladi)