Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-08 09:53:33    
Bangarori 2 na Cote d'Ivoire masu gwagwarmaya da juna sun yi shawarwari kan kwance damara

cri
Wakilan sojan gwamnatin kasar Cote d'Ivoire da tsohuwar kungiyar dakarun da ke adawa da gwamnatin wato jam'iyyar the New Forces sun yi shawarwari a birnin Yamoussoukro, hedkwatar kasar Cote d'Ivoire a ran 7 ga watan nan, inda suka yi tattaunawa kan maido da shirin kwance damara.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, babban makasudin shawarwarin da aka yi a ran nan shi ne tabbatar da jadawalin kwance damara. Bangarorin 2 da suka yi shawarwarin sun amince da kafa kwamitoci guda 2 na musamman, don sa idon kan kwance damara da tsara matakan tabbatar da lafiyar wakilan jam'iyyar the New Forces da suka shiga gwamnatin sulhuntawar al'ummar kasar. Wakilan sojojin kiyaye zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya da na kasar Faransa sun halarci shawarwarin nan.?Tasallah?