Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-05 11:23:55    
Shugaban kwamitin kungiyar AU ya bukaci kasashe masu arzikin masana'antu da su cika alkawarin yafe basussuka

cri
A birnin Syrte na kasar Libya, shugaban kwamitin Kawancen Kasashen Afirka Alpha Oumar Konare ya bayyana a ran 4 ga watan nan cewa, kudurin yafe wa kasashen mafi fama da talauci guda 18 basussukan da ake binsu da rukunin kasashen G8 masu arzikin masana'antu ya tsai da a kwanan baya, wani muhimmi da madaidaicin mataki ne da ya dauka, abin da ake fuskanta a yanzu shi ne tilas ne kasashe masu arzikin masana'antu su cika alkawarin da suka yi cikin tsanake.

Mr. Konare ya yi wannan bayani ne a lokacin da ya yi jawabi a gun bikin bude taron na 5 na shugabannin kungiyar AU a ran nan. Ya kara da cewa, ya kamata nan gaba a sa ido kan kasashe masu arzikin masana'antu wajen cika alkawarin da suka yi yadda ya kamata.

A sa'i daya kuma, a gun bikin bude taron, shugaban kasar Libya Muammar Al-Qadhafi ya bayyana cewa, kasashen Afirka sun yi wa kasashe masu ci gaban masana'antu godiya saboda taimakonsu, amma sun ki karbar taimakon da za a ba su tare da sharadi.(Tasallah)