Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-05 11:01:10    
ECOWAS ta kalubalanci bangarorin Guinea-Bissau da su maganci harkokin nuna karfin tuwo a lokacin babban zabe

cri

Babban sakataren mai cikakken iko na kungiyar ECOWAS Mohamed Ibn Chambas, wanda ke halartar taro na 5 na shugabannin kungiyar AU a birnin Syrte na kasar Libya, ya bayyana a ran 4 ga watan nan cewa, ya kamata bangarori daban daban na kasar Guinea-Bissau su maganci harkokin nuna karfin tuwo a cikin babban zaben shugaban kasar da za a gudanar a zagaye na 2 a ran 24 ga watan nan.

Sa'an nan kuma, Mr. Chambas ya kalubalanci sojojin kasar Guinea-Bissau da su tsaya matsayin 'yan ba-ruwanmu a cikin kada kuri'a a zagaye na 2 da za a yi, ya kuma yi kira ga bangarorin da suka shiga babban zaben da su girmama sakamakon babban zaben. Ban da wannan kuma, ya yi kashedi cewa, idan ana samun tashin hankali a kasar Guinea-Bissau, to, zai ba da tasiri kan kwanciyar hankali na duk yankin yammacin Afirka kai tsaye.(Tasallah)