Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-05 10:04:59    
Tilas ne a yi taka tsantsan wajen yin wa M.D.D. kwarkwarima, in ji ministan harkokin waje na Sudan

cri
Ministan harkokin waje na kasar Sudan Mustafa Othman Ismail da ke halartar taron shugabannin Kawancen Kasashen Afirka a birnin Syrte na kasar Libya ya bayyana a ran 4 ga watan nan cewa, yin wa Majalisar Dinkin Duniya kwarkwarima ya shafi moriyar bangarori daban daban, shi ya sa tilas ne a yi taka tsantsan wajen wannan.

Lokacin da yake zantawa da manema labaru a ran nan, Mr. Ismail ya jaddada cewa, ya kamata kasashen Afirka su sami kujerun din din din guda 2 a kwamitin sulhu na majalisar, sa'an nan kuma kasashen da aka kara a wannan gami su iya kin amincewa. Ya ci gaba da cewa, kasashen Afirka sun riga sun tattauna wannan batu a gun taron ministocin harkokin waje na kungiyar AU da aka yi kafin wannan, za su mika sakamakon karshe a gun taron shugabannin kungiyar AU da ake yi don kada kuri'a.(Tasallah)