Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-05 09:34:11    
Kawancen 'yan hamayya na kasar Mauritius ya ci nasarar babban zabe

cri
Kwamitin babban zabe na kasar Mauritius ya ba da sanarwa a ran 4 ga watan nan da dare cewa, kawancen 'yan hamayya wato 'kawancen al'ummar kasar' da jam'iyyar kwadago ke shugabanta ya ci nasarar zaben 'yan majalisar jama'ar kasar da aka yi a ran 3 ga watan nan.

Shugaban jam'iyyar kwadago Navin Ramgoolam zai sake zaman firaministan kasar bayan shekaru 5 da suka wuce, zai fara wa'adin aikinsa na shekaru 5. Shugaban kawancen rike da mulki na kasar kuma firaministan kasar na yanzu Paul Berenger zai zama dan majalisar jama'ar kasar a wannan gami. A cikin jawabin da ya yi a ran nan da dare, Mr. Berenger ya amince da cin tura, zai yi murabus nan da nan bayan da aka bayar da sakamakon babban zaben.(Tasallah)