Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-04 18:13:50    
Gwamnatin kasar Somaliya za ta bi shirin neman sulhu gaba daya a duk kasar

cri
A kwanan baya, firayin minista Ali Mohammed Gedi na gwamnatin rikon kwarya ta kasar Somaliya ya bayyana cewa, gwamnatinsa za ta bi shirin neman sulhu gaba daya a duk fadin kasar domin ingiza aikin shimfida zaman lafiya da dinkuwar duk kasar tun da wuri.

Lokacin da yake ganawa da manema labaru a wani ofishin wucin gadi a garin Jowhar da ke arewa da birnin Mogadishu na kasar, Mr. Gedi ya ce, a cikin makon da ake ciki, a yankuna 92 na duk kasar Somaliya, za a shirya tarurukan neman sulhu domin kafa ene ene a wadannan yankuna. Bayan watanni 2 masu zuwa, za a kira taron neman sulhu a larduna daban-dabam. Daga karshe, za a kira babban taron neman sulhu a duk fadin kasar a birnin Mogadishu, babban birnin kasar. (Sanusi Chen)