Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-07-04 11:46:09    
Mr. Mbeki ba ya da niyyar gyara tsarin mulkin kasar don zaman shugaban kasar a karo na 3

cri
Lokacin da yake zantawa da kafofin yada labaru a ran 3 ga watan nan da dare, shugaban kasar Afirka ta Kudu Thabo Mbeki ya bayyana cewa, ko da yake jam'iyyar ANC da ke mulkin kasar tana da matsayin rinjaye na samun kujaru da yawansu ya kai kashi 2 bisa 3 a cikin majalisar dokokin kasar, amma ba za ta gyara tsarin mulkin kasar don ya ci gaba da zaman shugaban kasar a karo na 3 ba.

Game da tambayar mutumin da zai zama shugaban kasar da kuma shugaban jam'iyyar ANC, Mr. Mbeki ya jaddada cewa, wannan yana dogara ga ra'ayoyin jama'ar kasar da dukan 'yan jam'iyyar ANC, ban da wannan kuma, yana ganin cewa, ba zai yiwu a warware wannan matsala kafin taron wakilan jam'iyyar ANC da za a yi a shekarar 2007 ba.(Tasallah)