Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-05-16 09:53:47    
Gwamnatin kasar Burundi da dakaru masu adawa da gwamnatin sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta

cri

Ran 15 ga wata, a Dar Es Salaam, fadar mulkin kasar Tanzania, gwamnatin wucin gadi ta kasar Burundi ta kulla yarjejeniyar tsgaita bude wuta da dakaru masu adawa da gwamnatin mai taken kungiyar 'yantar da al'umma, wato Force for National Liberation a bakin Turawa.

Bayan da Domitien Ndayizeye, shugaban kasar Burundi, da Agathon Rwasa, shugaban dakarun da ba sa ga maciji da gwamnati, suka yi zantawa, Therence Sinunguruza, ministan harkokin waje na kasar ya sanar da cewa, bangarorin 2 sun tsagaita wuta nan da nan, kuma za su kafa wata kungiya a cikin wata daya domin tabbatar da tsarin tsagaita wuta. Mista Sinunguruza ya yi nuni da cewa, bangarorin 2 za su yi shawarwari kan mayar da kungiyar 'yantar da al'umma daya daga cikin bangarori masu kula da aikin shimfida zaman lafiya a kasar Burundi. (Bello)