Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-29 13:52:02    
Jam'iyyun 'yan hamayya na Cote d'Ivoire sun yi maraba da shigar da shugabanninsu a babban zabe da shugaban kasar ya amince

cri
Jam'iyyun 'yan hamayya da rukunonin dakarun 'yan hamayya na kasar Cote d'Ivoire sun ba da sanarwar hadin gwiwa a ran 28 ga watan nan cewa, sun yi maraba da kudurin da shugaban kasar Laurent Gbagbo ya tsai da, wato ya yarda da 'yan takarar neman zaman shugaban kasar na dukan jam'iyyun da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a shekarar 2003, musamman ma shugaban babbar jam'iyyar 'yan hamayya Alassane Ouattara da su shiga babban zaben shugaban kasar a watan Oktoba na shekarar da muke ciki.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, aikin yunkurin shimfida zaman lafiya da sulhuntawa a kasar Cote d'Ivoire ya kawar da wani muhimmin matsala ne saboda kudurin da Mr. Gbagbo ya tsai da.(Tasallah)