Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-22 18:26:01    
An sassauta annobar Marburg a kasar Angola

cri

Ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Angola da Kungiyar WHO sun ba da rahoto kan annobar ciwon zazzabin ha'bo na cutar Marburg a ran 21 ga watan nan da dare, inda aka bayyana cewa, ba a kara samun mutumin da ya kamu da wannan ciwo a kasar Angola a cikin awoyi 24 da suka gabata ba, an sassauta annobar Marburg a kasar.

Rahoton ya bayyana cewa, ba a kara samun mutumin da ya kamu da irin wannan ciwo ba a lardunan Luanda da Cabinda da Cuanze Sul da Cianze Norte da Malanje da kuma Zaire a cikin kwanakin nan 4 da suka wuce a jere, an sassauta ciwon a wuraren nan.

Yanzu masana 40 a fannin aikin likitanci daga kungiyar WHO da kungiyar da ake kira 'doctors without borders' a turance suna ba da taimako ga ma'aikatar kiwon lafiya ta lardin Uige wajen yaki da annobar Marburg.(Tasallah)