Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-19 12:10:32    
An yi bikin ranar cikun shekaru 25 da aka samu 'yancin kan kasar Zimbabwe

cri

Ran 18 ga wata, a birnin Harare, fadar mulkin kasar Zimbabwe, mutane da yawa suka taru domin bikin ranar cikun shekaru 25 da aka samu 'yancin kan kasar.

Robert Gabriel Mugabe, shugaban kasar Zimbabwe ya yi jawabi a wurin biki, inda ya yi bitar fafutukar da jama'ar kasar suka yi domin neman samun 'yancin kan kasa, da kuma nasarorin da suka samu bayan samun mulkin kan kasa. Ya ce, bunkasa tattalin arziki shi ne babban nauyin da ke kan wuyan gwamnatin kasar. Domin yaki da takunkumin da kasashen yamma suka sanya wa kasar Zimbabwe, gwamnatin kasar za ta ci gaba da yalwata huldar da ke tsakaninta da kasashen Asiya da na Afirka, yadda za a raya tattalin arzikin kasar.

Ban da wannan kuma, Kennrth David Kaunda, tsohon shugaban kasar Zambia, wanda ya hallara a wurin bikin bisa gayyatar da aka yi masa, ya gaya wa maneman labaru cewa, kada a dogara a kan sauran mutane yayin da ake neman bunkasuwar nahiyar Afirka. Ya kamata, 'yan Afirka su hada kansu yadda za su raya nahiyarsu. (Bello)