Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-19 09:52:32    
Shugaban kasar Zimbabwe ya yi kira ga jama'arsa da su  hada kansu domin raya kasa

cri

Ran 18 ga wata, a kasar Zimbabwe, an yi bikin ranar cikun shekaru 25 da kasar ta sami 'yancin kai, inda shugaba Mugabe na kasar ya yi kira ga jama'arsa da su hada kansu domin raya kasa.

Ya ce, ana bukatar hadin kai ba ma kawai a lokacin da ake fafutukar neman 'yancin kan kasa ba, hatta ma a yayin da ake yaki da duhun kai da talauci da yunwa da kuma cututtuka.

Ban da wannan kuma, ya nuna cewa, idan ba tare da taimako da goyon baya da sauran kasashen Afirka suka bayar ba, kasar Zimbabwe ba zata samu 'yancin kan kasa ba. Jama'ar kasar Zimbabwe ba za su manta da wannan ba. (Bello)