Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-15 13:15:14    
Kamata ya yi kasashen Afirka su sami zaunannun kujeru 2 na kwamitin sulhu na M.D.D., in ji Mr. Mbeki

cri
Shugaban kasar Afirka ta Kudu Thabo Mbeki ya bayyana a birnin Capetown, hedkwatar kasar Afirka ta Kudu a ran 14 ga watan nan cewa, kamata ya yi kasashen Afirka su sami zaunannun kujeru guda 2 na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, ta haka kasashen Afirka za su kara taka rawarsu a cikin al'amuran kasa da kasa.

Mr. Mbeki ya ambaci yin gyare-gyare kan Majalisar Dinkin Duniya a cikin jawabin da ya yi a majalisar dokokin kasar a ran nan. Ya yi nuni cewa, ya kamata kasashen Afirka su sami kujerun din din din guda 2 a cikin kwamitin sulhu, haka kuma suna da ikon kin amincewa, wannan ya taka muhimmiyar rawa wajen aikin awar da talauci a duniya da majalisar take yi.(Tasallah)