Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-15 09:50:24    
Gwamnatin kasar Zambia ta bayar da gargadi na cutar Marburg

cri
A ran 14 ga wata, yayin da ministan kiwon lafiya na kasar Zambia Brian Chituwo yake amsa tambayoyin da kafofin watsa labaru suka yi masa, ya ce, gwamnatin kasar ta riga ta bayar da gargadi na cutar Marburg ga johohi 3 na kasar da ke iyakar kasa da ke tsakaninta da kasar Angola tare da daukan matakai domin hana cutar ta yadu zuwa kasar Zambia.

Mr Chituwo ya ce, ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar ta riga ta bayar da wajibabbun na'urorin asibiti ga jihohin 3 da ya ambata tun farko, kuma tana shirin koyar wa jama'ar wurin ilmin da abin ya shafa. Ban da wannan kuma, kasar Zambia tana yin mu'amala da kungiyar kiwon lafiya ta duniya, ta yadda za ta iya samun labarun da abin ya shafa game da cutar.(Danladi)