Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-14 09:13:43    
A kalla dai shugabannin kasashe 56 za su halarci taron Asiya da Afirka na karo na biyu

cri
A ran 13 ga wata, a birnin Jakarta, ministan harkokin waje na kasar Indonesia Hasan Wirayuda ya shelanta cewa, a kalla dai shugabannin kasashen Asiya da na Afirka 56 za su halarci taron Asiya da Afirka na karo na biyu wanda za a yi a birnin Jakarta daga ran 22 zuwa ran 23 ga watan nan da muke ciki, inda kuma za su tattauna maganar hadin gwiwa tsakanin nahiyoyin biyu a fannoni da dama.

A gun taron watsa labaru da aka shirya a ran nan, Mr.Wirayuda ya ce, mai yiwuwa ne za a kara samun mahalartan taron a kusantowarsa.

An ce, a gun taron nan na Asiya da Afirka, za a bayar da sanarwa da kuma tsarin ka'adojin aiki angane da kulla huldar aminci tsakanin Asiya da Afirka. Ban da wannan, a ran 24 ga wata, a birnin Bandung, za a yi bikin murnar cikon shekaru 50 da aka kira taron Asiya da Afirka na karo na farko, wato taron Bandung.(Lubabatu Lei)