Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-13 09:38:14    
Kungiyar WHO tana damuwa kan cewar ba a kebe wasu mutane wadanda suka kamu da cutar Marburg ba

cri

A gun taron maneman labaru da kungiyar kiwon lafiya ta WHO ta yi a ran 12 ga wata a birnin Geneva, Fadela Chaib, mai magana da yawun kungiyar ta yi nuni da cewa, kungiyar tana damuwa sosai kan cewar, har yanzu gwamnatin kasar Angola ba ta kebe wasu mutanen da ake tsammanin cewa sun kamu da cutar Marburg ba.

 Madam Chaib ta ce, a kasar Angola, an bar wasu mutanen da ake tsammanin cewa sun kamu da cutar Marburg a gidajensu, ba a kebe su a cikin asibiti domin binciken lafiyar jikinsu ba. Wannan zai haddasa kara yaduwar annoba a tsakanin al'umma, domin wadannan mutane ka iya yada cutar wa danginsu. (Bello)